Mata ta roƙi kotu ta raba aurenta da mijinta saboda sun kwashe shekaru 2 tare ba haihuwa


Wata matar aure mai suna Shakirat Ayinla, a yau Alhamis ta roki wata kotu da ke Centre-Igboro da ta raba aurenta bisa rashin haihuwa tsawon shekaru biyu da auren ta.
Ayinla ta shaidawa kotu cewa mijinta Jimoh ya dena sonta, daily Nigerian Hausa na ruwaito.
“Na yanke shawara a kan wannan batu. Ina son kotu ta raba auren mu,” ta shaida wa kotu.
Da yake mayar da martani, Mista Jimoh, ya shaida wa kotun cewa har yanzu yana kaunar matarsa duk da cewa har yanzu ba ta taɓa haihuwa ba.
“Muna zaune tare cikin lumana har zuwa wani lokaci a watan Yuli, lokacin da ta nemi tafiya arewa, don ziyartar ‘yar uwarta, domin ta ɗan samu sauyin mahalli bayan kasuwancinta ya rushe.
“Na yarda da ita kuma na ci gaba da tuntuɓar ta. Na rika aika mata da kuɗin abinci akai-akai. Na yi matukar kaɗuwa da na ji cewa ta dawo Ilorin amma ta ki dawowa gida na.
“Na kira ne don tabbatar da jita-jita amma ta musanta hakan daga baya ta amsa cewa ta dawo makonni hudu da suka wuce kuma ba za ta dawo gida na ba saboda ta gaji da aure na.
Alkalin kotun, AbdulKadir Ahmed, ya ce kotun za ta ba da shawarar cewa ma’auratan su yi kokarin sasanta rikicin da ke tsakaninsu.
“Kotu ba za ta tilasta wa kowane bangare su ci gaba da zaman aure ba,” in ji shi.
Ahmed ya dage sauraren karar har zuwa ranar 30 ga watan Nuwamba, domin samun rahoton sasantawar.