Labarai
An fara zanga-zangar matsin rayuwa a Neja har matasa sun rufe babban titin Abuja – Kaduna


Advertisment
Fusatattun matasa a ƙaramar hukumar Suleja a jihar Neja sun yi tsinke a kan tituna domin zanga-zangar matsin rayuwa a Nijeriya .
Masu zanga-zangar sun rufe babban titin Abuja zuwa Kaduna a safiyar yau Litinin.
Tuni fusatattun matasan su ka riƙa daga kwakayen masu rubuce-rubuce daban-daban kamar su “mu ba bayi ba ne”, “tura ta kai bango”, “a janye manufofin da ke gallazawa talaka”, “a dawo da tallafin man fetur” da sauran su.
Zanga-zangar ta yi riga malam masallaci domin saura kwano uku a fara zanga-zangar matsin rayuwa da aka shirya a fadin kasar.
Daily Nigerian Hausa
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)




