AddiniLabarai

Zanbada Naira Milion 1 Ga Duk Wanda Yakawo Mana Inda Manzon Allah Yayi Wa’azin Kasa – Imam Dr. Hamza Assudaniy Zaria

Advertisment

A cikin wannan sati ne da kungiyar izalah ƙarƙashin jagoranci Sheikh Abdallah bala lau sunka shirya wa’azin kasa a garin zaria da ke jihar kaduna wanda an shafe shekaru kusan takwas rabo da ayi wa’azin kasa da kasa a cikin garin zaria.

Shine yanzu muke samun wani labari inda wani malamin yake ƙalubalarntar wa’azin kasa da kungiyar izalatul bidi’a wa’ikamatus sunnah suke shiryawa a matsayin bidi’a amma suke cewa sune yan bidi’a masu Maulidi.

Zanbada Naira Milion 1 Ga Duk Wanda Yakawo Mana Inda Manzon Allah Yayi Wa'azin Kasa - Imam Dr. Hamza Assudaniy Zaria
Zanbada Naira Milion 1 Ga Duk Wanda Yakawo Mana Inda Manzon Allah Yayi Wa’azin Kasa – Imam Dr. Hamza Assudaniy Zaria

Malam Imam a Sheikh ya fitar da Wannan abun ne a shafinsa na facebook mai suna Imam Dr.Hamza Assudaniy, inda yake cewa.

“Anata Bidi’antar Da Murnan Samun Manzon Allah Wanda Akafi Sani Da (MAULIDI) Ga Babban Bidi’a Na Kewaye Daku

Advertisment

Wa’azin Kasa Bidi’a Ne Annabi Bayyiba Sahabbai Basuyiba Tabi’ai Da Tabi’ut Tabi’una

Tabbas Idan Baku Kawo Mana Inda Sayyuduna Muhhammadu Rasulullahi Yayi Ba Kun Tabbatar Mana Ku Yan Bidi’a Ne

Muna Rokon Allah Ka Dauwamar Damu Cikin Soyayyar Manzon Allah”

A yau ne ranar Assabar kungiyar izalatul bidi’a wa’ikamatus sunnah sunka shirya wa’azin kasa da kasa a cikin garin zaria , da za’a gudanar a yau kamar yadda shafinsu sunka wallafa sun kamala shirye shirye tsaf domin fara wannan karatu.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Advertisment
Back to top button