Labarai

Sojoji sun gano wata ‘yar makarantar Chibok da aka sace tare da jaririnta a Borno

Advertisment

Sojojin Najeriya sun gano wata Hauwa Joseph, wadda a cewarsu tana daya daga cikin ‘yan matan da aka sace daga makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke garin Chibok a Jihar Borno a ranar 14 ga Afrilu, 2014.jaridar LIB na ruwaito

 

Rundunar sojin a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafukanta na sada zumunta a ranar Alhamis, 16 ga watan Yuni, ta ce an gano Hauwa da jaririnta a wani samame da suka kai a Borno.

 

Sojoji yayin aikin share fage a ranar 14 ga watan Yunin 2022 sun kama wata yarinya da aka sace daga GGSS Chibok mai suna Hauwa Joseph, wadda Boko Haram suka yi garkuwa da ita a ranar 14 ga watan Afrilun 2014. Yarinyar Chibok da aka kama tare da jaririnta a halin yanzu suna wani asibitin sojoji.” sanarwar ta karanta. 

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button