Bayan Kashe Al’umma Da ‘Yan Bindiga Suka Yi A Yankin Shanga Dake Jihar Kebbi, Sun Sake Dawo Sun Bankawa Wani Kauye Wuta (bidiyo da hotuna)


Dukiyar al’umma da kuma abincinsu duk sun salwanta, yayinda al’ummar kauyen kowa ya tsere domin tsira da rayuwarsu.
Har yanzu dai cikin zancen al’umma wannan yankin suna cikin fargaba a wannan karamar hukumar mulki ta Shanga. Wanda ake duban cewa matukar ba jami’an tsaro suka kawo dauki ba to tabbas zasu Kara aikata wani mummunar ta’adin.
~Yushau Garba Shanga.










Irin yadda talakkawan arewa ke cigaba da dandana kudarsu kenan a hannun makiyan Allah.
Akwai ire Iren TUNGAR ZARUMAI sunfi dubu da yanfashin daji suka Kona tareda kashe mutane da sace wasu domin naiman kudin fansa.
Ina hasashen tabbas Nan gaba kadan Nigeria kancokam ka iya komawa kamar kasar mexico a baya tabbas idan kuwa wannan hasashen ya tabbata to tabbas masu mulki sunyi bankwana da runtsa idanunsu da sunan barci.
Lallai a irin wannan yanayi na kisa da gadara da yan”taadda sukeyiwa al’ummar arewacin Nigeria abun Allah waddaine.
Mustapha sarkin kaya ya wallafa bidiyon a shafinsa na Facebook.



One Comment