Labarai

Ƴan bindiga sun ƙona mata da sirikarta da yara biyu a Sakkwato

Advertisment

Wasu ƴan bindiga sun kona wata mata tare da da sirikarta da kuma ‘ya’yanta biyu da ransu a wani harin da suka kai a garin Sakkwato.

Daily Nigerian ta rawaito cewa an ce ƴan bindigar sun kai harin ne a kauyen Kurya da ke karamar hukumar Rabah a jihar da misalin karfe 8:30 na yammacin ranar Lahadi, inda suka kashe mutanen kauyen 12 tare da sace mata uku.

Wani mazaunin yankin, Yusuf Garba ya ce daya daga cikin wadanda aka sace ta rasa mijinta a harin.

Ƴan bindiga sun ƙona mata da sirikarta da yara biyu a Sakwkwato
Ƴan bindiga sun ƙona mata da sirikarta da yara biyu a Sakwkwato

“Daga cikin wadanda aka kashe akwai wata mace daya da aka kona ta mutu tare da surukarta da ‘ya’yanta biyu a cikin dakinsu,” in ji shi.

A cewarsa, daga baya maharan sun yi wani kazamin fada da sojoji.

“Muna zargin su ma sun yi asara mai yawa saboda mun ga jini a inda suka ajiye babura. Amma kun san ba sa barin gawarwakinsu a baya,” inji shi.

Sai dai rundunar ƴan sanda a jihar ta tabbatar da mutuwar mutane bakwai yayin harin.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Sakkwato, ASP Ahmed Rufa’i, ya kara da cewa suna ci gaba da

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button