Na biya G-fresh Al’ameen maƙudan kudi ya sake ni, Babu aure ni da shi – Sadiya Haruna


Idan baku manta an dade ana dambarwa aure tsakanin Al’ameen G-fresh da sayyada sadiya haruna wanda har abun yaje har gaban kotu wanda anka nemi sasancin tsakanin ma’aurata biyu.
To a yau shine gidan rediyo freedom sun samu zantawa da ita amarya sayyada sadiya haruna akan makomar aurensu yake domin har yanzu, shi angon Al’ameen G-fresh yana iƙirarin matarsa ce.
Freedom Radio ta yi ƙoƙarin jin ta bakin G-Fresh sai dai har kawo lokacin haɗa wannan rahoto ba mu same shi ba.
Ga abinda take cewa a cikin wani sautin murya.
Ana rade raden Shari’arku da G-fresh yazo karshe minene ya faru ?
“Eh Shari’a yazo ashe malam garba akan dubu ɗari biyar ne ₦500,000 ne yake wahalda Shari’ah kullum yace yana son matarshi yaki fito mana a mutum amma Alhamdullahi wanann karo ya fito a mutum matsalar sa dai dubu ɗari biyar ne na bashi, kamar yadda ya furta a baki ya ƙara rubuta takarda a rubuce bani ba shi har abada.
Ina masa fatan alkhairi Allah ya hada kowa da dai-dai sa.
Yanzu kenan za’a ce ba kare bin damo ba maganar biko?
Haba kai ko auren da anka shafe wata takwas ba’a tare , ba’a taɓayin kwana daya na farin ciki ba, ina zancen biko a wannan lamari kamar dai yadda na gayamaka Allah ya hada kowa da rabonsa, Allah ya hada kowa da dai-dainsa na masa fatan alkhairi.-inji sadiya haruna.
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)




