Labarai

El-Rufai Ya Shirya Yin Fada da Gwamnatin Shugaba Tinubu

Advertisment

Watanni takwas bayan da majalisar dattawa ta ki amincewa da shi, rahotanni sun ce tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, zai fara taƙaddama da gwamnatin Bola Tinubu Duk da cewa suna jam’iyya ɗaya, akwai alamun cewa El-Rufai da Shugaba Tinubu ba aminan juna ba ne Bayan da aka hana shi damar zama minista a 2023, haɗe da jita-jitar da ake yaɗawa na cewa yana sha’awar shugabancin Najeriya a 2027,

El-Rufai ya yanke shawarar ɗaukar mataki

Nasir Ahmad El-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kaduna yana shirin “yaƙi” da Shugaba Bola Tinubu a aƙalla kotuna biyu. Kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito a ranar Asabar, 6 ga watan Afrilu, za a gabatar da faɗan ne a kotunan Najeriya.

El-Rufai na sa ran wanke sunansa daga zargin cewa yana da hatsarin tsaro wanda ya hana shi samun muƙamin minista.

Meyasa El-Rufai zai je kotu?

Tsohon gwamnan yana son wanke kansa ne bayan da wasu masu sharhi suka ce zai ƙalubalanci sake tsayawa takarar Shugaba Tinubu a 2027.

Rahotanni sun ce na kusa da El Rufa’i sun bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta wulaƙanta tsohon gwamnan a bainar jama’a.

Rashin samun muƙamin na El-Rufai ya ba na kusa da shi mamaki duba da irin rawar da ya taka wajen sanya gwamnonin Arewacin Najeriya suka marawa Tinubu baya a lokacin zaɓen 2023.

Jaridar Vanguard ta ambato wani na kusa da El Rufai yana cewa: “Kuna tunanin cewa Mallam zai bari wannan tambarin ya tsaya a kansa? Ina mai tabbatar muku da cewa zai wanke sunansa a gaban kotu.”

– Liberty Tv

Advertisment






Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button