Labarai

Cire tallafin mai: Masu sana’ar fata sun koka kan karancin Kwastomomi a kano

Advertisment

Tabarbarewar tattalin arziki sakamakon cire tallafin man fetur ya yi matukar tasiri ga karuwai a jihar Kano yayin da suke koka kan rashin samun kwastomomi a yanzu, Vanguard ta tattaro. Sun bayyana bacin ransu ne a lokacin da suke amsa tambayoyi wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a unguwar Sabon Gari da ke karamar hukumar Fagge a ranar Lahadi.

Karuwan a cikin tsohon birni Kano, wadanda a baya suke cike aljihu da kudi tare da yanga yanzu sun koma neman abokan assha ido rufe saboda tsananin talauci.Legit na tattaro labarin.

Yadda matsin tattalin arziki ya shafi karuwai

Mercy Benjamin ta shaida wa NAN cewa kafin yanzu, a baya suna samun kwastomomin wucin gadi d ake iya ba da N5,000 kowanne awa daya, amma banda yanzu da aka cie tallafin mai.

Cire tallafin mai: Masu sana'ar fata sun koka kan karancin Kwastomomi a kano
Cire tallafin mai: Masu sana’ar fata sun koka kan karancin Kwastomomi a kano Hoto: facebook

Ta kara da cewa, a yanzu kwastomomin ba sa biyan sama da N500 zuwa N700 a kowane awa daya tsabar fatara.

Wata ‘yan gidan magajiya, wacce ta bayyana kanta da Jennifer, ta shaida wa NAN cewa yanzu dai harkar ta su ba ta kawo wuta, komai ba ya motsi a bangarensu.

Kwastoman N20,000 sun koma ba da N1,500 Ta kuma bayyana cewa, akwai kwastomomin da a baya ke biyansu N20,000 a kwana dasu tare da daukar nauyin wurin kwana da abincinsu, amma yanzu N1,500 ma ba sa samu, Royal Times ta tattaro.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button