Soyayyar Rakiya Da Breaker Ni GANAU Ba Jiyau Ba – cewar wani matashi ya bada labari mai ban mamaki
Da fari dai ban so na saka baki na akan maganar nan ba kwata-kwata, saboda a wajena, ba kowane batu ne ya ke buΖatar tankawa ba. To amma abubuwa biyu sun ja hankali na Ζwarai da gaske. Abu na farko shi ne tausayin da Rakiya ta bani, ta kuma bawa mutane da yawa bayan kallon hirar su da na yi da Hadiza Gabon. Sai abu na biyu yadda na ga wasu na alaΖanta cewa wannan masoyin ba wani ba ne illa Hamisu Breaker. Mu’azu suleiman sa’eed ne ya bada wannan labarin a shafin na facebook
Wannan gaΙar ta biyu ta yi daidai da tunanina bayan kammala kallon hirar da muka yi tare tawa masoyiyar da bamu wahalar da juna ba????. Ina gama kalla, nace mata, Allah ya sa ba BREAKER ta ke nufi kuwa. Ummu Hanan tace anya kuwa?

Mu dawo maganar mu. A ΖarΖashin wannan gaΙa ta biyu ina da abubuwan faΙa dozin guda kamar haka:
1. Ban yi wannan rubutun domin aibata wani ko bawa wani kariya a cikin su biyun ba. Illa dai kawai na Ιan san wani abu dangane da alaΖar su biyun.
2. Hamisu maΖobcin mu ne a unguwar Dorayi, domin gida Ιaya ne tsakanin mu da gidansu, don haka tamkar Ζani ya ke a wajena tun bai kai shekara biyar a duniya ba. Bayan kasancewarsa maΖobcin kuma tamkar Ζani, Hamisu Ιalibi na ne na tsawon shekaru kafin yai nisa a harkar waΖa, domin kuwa har ya fara waka yana koyar karatu a wajena.
3. Ban san abin da ya fara haΙa Hamisu da Rakiya ba, amma na tabbatar cewa Rakiya ta yiwa ko kuma tana yi wa Hamisu so maras misaltawa, domin kuwa ta kan zo ta wuni a gidansu tare da mahaifiyar sa, su yi hira, ta taya ta aiki, kuma ta raka Ζanwarsa Khadija duk inda aka aketa (kanti, siyo kayan miya da sauransu), duk da kasancewar matsayinta na tauraruwar fim (ko nace celebrity).
4. Ba sau Ιaya ba, ba kuma sau biyu ba, duk lokacin da na shiga gidan su Hamisu na sameta (Rakiya) ko suka fito da Khadija ko da shi Hamisu, in har Hamisu zai gaisheni to sai ta rusuna take gaishe ni. Saboda duk wanda ta fahimci yana da wata Ζima ko influence akan Hamisu tana girmama shi.
5. Ba ni kaΙai ba, duk waΙanda suke rukunin gidanjenmu sun saba da ganinta domin a wancan lokacin ΙaiΙai ne ranekun da bata gidan su Breaker (ko da baya gari).
6. Tambayar a nan shi ne, shin Hamisu Breaker ya taΙa soyayya da Rakiya?
7. Ba zan iya amsa tambayar kai tsaye ba, amma tun a wancen lokacin, abin da mafi yawan mu muka fahimta shi ne Rakiya ke neman soyayyar Hamisu Breaker. Kuma ina da dalili.
8. Na taΙa tattaunawa da shi a kan alaΖarsa da Rakiya, musamman akan zuwan da ke gidansu na rashin dacewar hakan. A lokacin ya bani amsar cewa tana sonsa ne, shi kuma gaskiya bai aminta ba. Ta kan zo gidan har ta tafi basu haΙu ba, domin ita tana zuwa wajen mahaifiyarsa ne da niyyar kamun Ζafa. Don haka ba yadda zai iya hana ta zuwa, saboda ya faΙa mata bata ji ba. Mun yi makamanciyar wannan maganar da mahaifiyar Hamisu watarana, kuma amsar da na samu bata ci karo da abin da Hamisu ya faΙa min ba.
9. Kamar yadda na ji (daga wasu abokansa) cewar akwai waΖoΖin da sukai tare da Hamisu wanda ita ta Ιau nauyin su, ta biya shi, ta kuma roΖe shi su yi video Ιin waΖar tare.
10. A lokacin da duk waΙannan abubuwan suke faruwa, Hamisu bai yi shura an san shi a ko ina kamar yanzu ba. Don haka in dai ya tabbata shi ne wanda Rakiya ta ba da labari, to tabbas ba Ιaukaka ce ta raba su ba, tun farko ta gino soyayyar ta ne da tubalin toka, ko kuma son maso wani.
11. Na iya tunawa a cikin hirarta akwai inda tace “Ya yi min duk wani abu da ya kamata na rabu da shi, na ma manta da shi a rayuwa ta, amma ban rabu da shi ba”. Idan har ya tabbata Breaker ne take nufi, to tabbas ni kai na naga dagiyar ta a irin yadda tun yana kulata, har ya zama yana sha mata Ζanshi, da mu’amalar da za ta rabu da shi Ιin amma bata dena ba.
12. A taΖaice, ba ina ganin laifin Rakiya ba ne, domin sha’anin so ya fi ga haka. Haka kuma ba ina kare Hamisu ba ne, amma ni ganau ne cewa tun ba a san Hamisu Breaker sosai ba, ya nuna rashin karΙar soyayyar Rakiya, don haka rabuwar su ba ta da alaΖa da matsayin da ya samu a rayuwa.
Ina Ζara tausaya mata matuΖar gaske, ina kuma yi wa dukkan masoya fatan Allah ya haΙa su da masoyansu na gaskiya (a cikin aure).






