Sarkin waka Nazir M Ahamd yayi Raddi Mai zafi kan Maganar wata jaruma da tace a daina haihuwa
Sarki Waka Nazir M Ahamd yayi raddi mai zafi kan maganar wata jarumar Kannywood tayi na cewa mutane su daina haihuwar yayanda basu iya kula da su.
Wanda wannan maganar da Jaruma Nafisa Abdullahi tayi anyi ta cece kuce akanta a dandalin sada zumunta na twitter inda shi kuma sarkin waka a yanzu nan ya fitar da magana mai zafin gaske wanda bai kira suna ba amma hausawa kance kowa yayi zagi a kasuwa yasan da wanda yake ga abinda yake fadi.
“Ba Almajirai Ne Yaran Da Iyayensu Suka Haifa Suka Kasa Kula Da Su Ba. Idan Kana Neman ‘Yayan Da Iyayensu Suka Kasa Kula Dasu, To Ka Taho Masana’antar Fim.”
Wannan shine gaskiya malanmai
Ko tayi dadi ko kar tayi dadi..
Ayi hakuri damu! pic.twitter.com/64wVl4lBHK— Sarkinwaka (@real_sarkinwaka) April 22, 2022
Nan take mutane sun fara tofa albarkacin bakinsu akan wannan magana da sarkin waka yayi.
@Mustapha bin isah : Wannan gaskiya ne
@real_sarkinwaka
Allah yasa su gane suma sugyara har karsu.
@commissioner : Kunfi kusa, Bama Shiga Fadan Cikin gida, Dan in kana shiga fadan cikin gida wata rana zaka ji kunya, Kuje cen ku karata…
@gaskiya tsirara : Subhanallahi ranka ya dade cikin martabawa da nuna girma zakasa su fara gaya maka bakakyan maganganu ????
Sarkin waka ya ƙara da cewa sun san salon yaurdara da sherin da ake laƙawa sunan Almajiranci da iyayensu.
To mu munsan abunda kuke kira da almajirci duk da ba sunansa kenanba musan niyyar da ke sa iyaye su kai yayansu mun kuma ga amfaninsa, wato kunfiso a bar yara a daji babu manufa aiyita basu bindigu suna kashe mune wannan shine burinku??
wannan shine kawai.
Ayi hakuri damu!— Sarkinwaka (@real_sarkinwaka) April 22, 2022