Wata Matashiya ta yiwa ƙawarta Yankan Rago A Kano


Wata matashiya da ke unguwar Maidile anan Kano ta kashe ƙawarta ta hanyar yi mata yankan rago.
Lamarin dai ya faru ne bayan da rigima ta kaure a tsakaninsu a daren ranar Alhamis.
Kamar yadda freedom radio fm na ruwaito. Tun da fari matashiyar da ta aikata kisan ta jife kawarta ta mai suna Bahijja da kalmar “Karuwa” inda ita kuma Bahijja ta mayar da martani.
Daga nan ne rikici ya kaure a tsakanin su, kuma nan take ƙawar ta ɗauko wuƙa bai Bahijja har gida tare da yi mata yankan Rago.
Sai dai ko da aka garzaya da Bahijja Asibiti don samun taimakon gaggawa tuni rai yayi halin sa.




Allahu Akbar anyi Jana’izar bahijja kenan wadda kawarta ta kashe ta.






