Bidiyo : Sheikh Kabiru Gombe Ya Baiwa Buhari Da Shuwagabani shawara a wajen Tafsir


A wajen darashin tafsirin da yake gabatar wa, Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe, ya yi kira ga shugaban Najeriya ya buda baitul-malin gwamnati.
Kabiru Haruna Gombe ya bukaci shugaban kasa da kuma gwamnonin jihohi su fito da kudi da nufin ba talakawa kayan abincin da za su ci a watan azumu.
“A bude baitul-mali, a saya wa talakawa tireloli na kayan abinci; shinkafa ta rika yawo, ana ba talakawa.”
“Ya ku gwamnonin jihohi, ku bude baitul-mali, a saya wa talakawa abinci a lokacin Ramadan. A fitar da dukiyar talakawa, a saya masu abinci saboda Allah.”
Shararren malamin kungiyar Jama’atul Izalatul Bidi’at wa Iqamatus Sunnah ya ba gwamnatin kasar shawarar yadda za a magance matsalar satar mutane.
Sheikh Gombe ya ce: “Masu garkuwa da mutane sun addabe ku, su na ta kashe miliyoyi a kan tsaro domin ku tsare al’umma, amma har yau babu nasara.”
“Ga hanya mai sauki da za ku yi nasara, ku ji tausayin na-kasa, idan ku ka yi haka, Allah zai ji tausayinku.”
Ga bidiyon nan kasa wanda malam ke fadi daga bakinsa.
Allah yasa a gwada @Waspapping_ Malam ya fita?? pic.twitter.com/tb6ewhpwin
— Yalli Najib (@najeeb_42743) April 29, 2021
Sakataren na Jama’atul Izalatul Bidi’at wa Iqamatus Sunnah wanda aka fi sani da Izala, ya ce idan shugabanni su ka tausaya wa talakawansu, to Allah zai jikansu.
Malamin ya yi wannan bayani ne a tafsirin da yake gudanar wa na a bana tare da Alaranma Ahmad Sulaiman a masallacin ‘Yan lilo a Tudun Wada, Kaduna.




