Kannywood

Wata Sabuwa! Ali Jita na fargbar dokar kulle saboda ‘ya ci kudin waka’

Advertisment

Yan Najeriya da dama na fargabar sake shiga dokar kulle irin wadda aka sha ta tsawon makonni a baya, ciki har da mawakin Hausa Ali jita.
Shahararren mawakin ya bi sahun ‘yan Najeriya a shafukan zumunta yana rokon a jinkirta saka doar kullen cutar korona “saboda ba ya son mayar wa mutane kudinsu na waka da ya riga ya karba”.
“A bari sai watan Maris kafin a saka dokar kulle, rayuwar mawaka na da muhummanci, ba zan iya mayar wa da mutane kudinsu ba, na gama shiri da kashe kudi,” in ji shi cikin wani sakon Twitter.
Kamar yadda bbchausa na ruwaito, kara da cewa da ma tuni mawaka sunka shiga matsin rayuwa tun daga farkon wannan shekara.
Dubban ‘yan Najeriya ma na ta bayyana ra’ayoyinsu game da dokar kullen, wadda gwamnatin tarayya ta sake bullo da wasu a jiya Litinin biyo bayan karuwar masu kamuwa da cutar korona.
Kalmar “lockdown” wato “kulle”, tana cikin abin da ‘yan Najeriya suka fi tattaunawa a kai a dandalin Twitter yanzu haka.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button