Addini

Shin wanda Yake Aikin Gwamnati Ya Hallata Ya Nemi N-Power ? ~ Dr Jamilu Yusuf Zarewa

Advertisment

Tambaya:
Assalamu Alaikum
Dr. Barka da Rana, Maganar N-Power ce. Yana hallata ga wanda yake aiki a state Government karamin ma’aikaci ya nemi aikin N-Power, don samun Karin abinda zaiyi amfani dashi?
Allah ya kara lafiya da ilimi mai amfani.

Amsa
Wa alaikum assalam
A zahiri bai halatta ba, saboda an tanadi N-POWER ne saboda wadanda ba su da aiki, don a rage musu radadin talauci da zaman banza da rashin abin Yi !!
Dukiyar Gwamnati ta Jama’ar kasa ce, wannan yasa Gwamnati ta yi tsarin da kowa zai amfana.

Wanda ya ji tsoran Allah, tabbas Allah zai azurta shi ta inda ba ya zato, wanda ya ci hakkin da ba na shi ba, Allah zai iya hada shi da wahala.

Allah ne mafi Sani

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

30/06/2020

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button