Labarai

CORONA: Gwamna Ganduje Ya Cire Dokar Kulle Gaba Daya A Jihar Kano

Advertisment

Daga Abdulrashid Abdullahi, Kano

Rahotanni daga jihar Kano na cewa Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Dakta Abdullahi Umar Ganduje ta janye dokar kulle da ta sanya a jihar don gudun yaduwar cutar Corona.

Bababban sakataren yada labarai na Gwamnan Kano Malam Abba Anwar shi ya bayyana haka a wata takarda da aka rabawa manema labarai.

Gwamnatin ta ce ragowar ranakun da ake kulle a Kano na Alhamis da Asabar da Talata an janye dokar gaba daya sakamakon yadda al’umma suke takura saboda dokar.

Ganduje ya yi kira ga al’ummar jihar Kano da su ci gabada bin matakan kariya da likitoci suka bayar.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment






Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button