Addini
Mata Uku Sun Karbi Musulunci A Garin Tilden Fulani
Advertisment
Daga Ibrahim Bangis Tilde
A yau Laraba (18/10/2017), an samu wasu mata guda uku da suka musulunta a cikin garin Tilden Fulani dake karamar hukumar Toro a jihar Bauchi.
Bayan sun musulunta an sauya musu suna kamar haka;
1. Maryam, a da sunanta Monica.
2. Khadija, a da sunanta Blessing.
3. Hafsa, wacce ta ke karamar yarinya ce, ita ma a da sunanta Nancy.
An gudanar da wannan aikin lankwanta masu kalmar shahada ne karkashin jagorancin Shugaban Majalisar Malamai na reshen Tilden Fulani, Mal Abdullahi Adam tare da rakiyar wasu fitattun mutane a cikin garin Tilde.
Ku na iya ganin wadannan mata yayin da su ka karbi shahada yau a gidan Garkuwan Yamini Alh Aliyu Tasshaqu.
Allah ya tabbatar da dugaduganmu a cikin addinin Musulunci, amin.
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com








![[Tafsirin Surah Âl-`Imrân:] - Dr Muhammad Sani Umar R/Lemo](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2022/04/FB_IMG_1649081565215.jpg?resize=390%2C220&ssl=1)