Labarai

Ana barazanar daina kai tumatur daga arewacin Najeriya zuwa kudu

Advertisment

Kungiyar dillalan tumatir da hadaddiyar kungiyar masu safarar kayan abinci da dabbobi ta Nijeriya, na barazanar daina kai tumatir a jihar Lagos.

Hakan ya biyo bayan zargin wulakanta musu kaya da suka ce ana yi.

Alhaji Ahmad Alaramma, shugaban kungiyar dillalan tumatir din ne ya sanar da hakan a taron manema labarai da suka kira a Zaria jihar Kaduna.

Ya ce lamarin da ya faru a kasuwar Oke-Odo a jihar Lagos ya jaza an lalata musu ‘kiret’ kusan 60,000 na tumatir, saukin ma, babu tumatir din a ciki.

Majiyarmu ta samu labarin daga Dclhausa cewa, ya ce ana sayar da kowane ‘kiret’ daya na tumatir a kan kudi N6,000, da yanzu haka mambobin kungiyar sun yi asarar kudin da suka kai N360m.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button