Labarai

Bidiyo : An kai hari gidan Talabijin na TVC a Legas

Wasu da ake zargin ‘yan daba ne sun kai hari a gidan talabijin na TVC da ke Legas.

Wata ma’aikaciyar gidan talabijin ɗin ta wallafa a shafinta na Twitter cewa suna cikin gabatar da shiri kai tsaye dole suka katse sakamakon ‘yan daban da suka faɗo daƙin gabatar da shirye-shiryen na su.

A halin yanzu dai gidan talabijin na TVC ɗin ya ɗauke, ma’ana ba a nuna tashar.

Rahotanni na nuna cewa gidan talabijin ɗin mallakar tsohon gwamnan Legas ne Bola Ahmed Tinubu, duk da cewa bai fito fili ya gasgata cewa shi ne ainahin mamallakin gidan talabijin ɗin ba.

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button