Uncategorized

Wata Sabuwa ! Akwai Matukar Darasi A Cikinsa: Auren Wasa Na Shirin Zama Gaskiya

Advertisment

Wani al’amari mai kama da wasan kwai-kwayo ya faru a garin Kontagora dake Jihar Neja wanda a yake dab da tabbata gaskiya, al’amarin da aka fara a matsayin wasa a shekaran jiya Litinin yanzu ya kai ga sanya ranar ɗaurin aure wanda a wannan Asabar ake shirin ɗaura masu aure a garin Libele Insha Allah.

Jamilu da Nasiba sun haɗu a garin Kontagora a ranar farko inda ƴar ƙaramar muhawara ta kaure tsakanin su akan al’amarin da ya shafi aure wanda take ganin bazai iya auranta ba inda shi kuma yasha alwashin zai iya auran ta muddin tace tana son shi duk da bai shirya yin aure ba, inda ta amsa cewa ita fa da gaske takeyi kuma ta amince zata aure shi nan take abokai suka haɗa kuɗin sadaki kuma aka tunƙari iyayenta suma iyayen sun amince tare da murnar da jin hakan wanda yanzu al’amari ya kankama ana dab da shan biki.

Yanzu haka abokan ango har sun tanadi ɗakin da za’a sanya amarya tare da cigaba da shirye shiryen shagulgulan biki, yayin da suma bangaren amarya suke cigaba da nasu hidimomi akan auran. Da haɗuwar su zuwa ranar aure kwana biyar, kuma yanzu sun tabbatar da suna son junan su tsakani da Allah.

Tsakanin Ango da Amarya waye za’a ce ya tsinci dami akala?

Wani fata zakuyiwa waɗannan ma’aurata

Daga:Comrade-Zakari Y Adamu Kontagora

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button