Labarai

Kotu ta yanke wa Sadiya Haruna hukuncin komawa Islamiyya

Advertisment

Yau Litinin rundunar ƴan sandan jihar Kano ta gurfanar da wata mai amfani da kafafen sada zumunta Sadiya Haruna a gaban kotu.
An gurfanar da ita a kotun shari’ar Musulunci da ke hukumar Hisbah, bisa zargin yaɗa batsa a kafafen sada zumunta.
Yayin zaman kotun mai shari’a Ali Jibrin Ɗanzaki ya yanke mata hukuncin sanyata a makarantar Islamiyya ta Darul Hadith har tsawon wata shida.
Kamar yadda freedom radio na ruwaito. Za ta riƙa zuwa kullum tare da rakiya jami’in hukuma.

Kotu ta yanke wa Sadiya Haruna hukuncin komawa Islamiyya
Kotu ta yanke wa Sadiya Haruna hukuncin komawa Islamiyya
Hoto : Instagram
Daga: sadiya haruna

Sannan za ta riƙa sanya hannu a duk sanda ta je.
Sadiya Haruna dai ta shahara a kafafen sada zumunta wajen yaɗa hotuna tare da kalaman batsa.
Kotu ta yanke wa Sadiya Haruna hukuncin komawa Islamiyya
Kotu ta yanke wa Sadiya Haruna hukuncin komawa Islamiyya Hoto :Instagram Daga sadiya haruna

Tun da farko rundunar ƴan sandan jihar Kano ce, ta karɓi ƙorafi daga mutane kan ayyukan matashiyar.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button