Labari Mai daɗi: Za’a sake ɗaukar sababbin N-power – Dr. Betta Edu


Ministar harkokin jin kai da rage radadin talauci Dr Betta Edu, ta ce ana shirin yin kwaskwarimar shirin N-Power domin daukar karin mutane da kuma tabbatar da biyan kudaden alawus-alawus din, wadanda suke amfana da shirin cikin gaggawa, kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito yanzu.
Ministar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa a yau Lahadi, da ta gabatar ta hannun mai ba ta shawara ta musamman kan harkokin yada labarai Rasheed Zubair, a Abuja.
Sanarwar ta ruwaito ministar na cewa nan ba da jimawa ba za a magance kalubalen da masu cin gajiyar N-Power ke fuskanta ta fuskar jinkiri wajen biyan kudaden alawus din su, da kuma daukan sabbin ma’aikatan N-Power din.
Ministar ta kuma ce ma’aikatar ta shirya samar da cibiyoyin jin kai a fadin kananan hukumomi 774 na kasar, inda ta kara da cewa za ta kasance cikin gaggawa wurin kawar da talauci a Najeriya.
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)





