Labarai
Kotu ta ayyana Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Kano


Advertisment
Kotun sauraron ƙarar zaɓen gwamnan Kano ta soke nasarar Abba Kabir Yusuf, a matsayin halastaccen gwamnan jihar.
Haka zalika, ta ayyana ɗan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya ci zaɓen gwamnan Kano na ranar 18 ga watan Maris ɗin 2023.
Jaridar BBC Hausa na ruwaito.Jam’iyyar APC ce ta shigar da ƙara a gaban kotun, tana ƙalubalantar nasarar Abba Kabir, bayan hukumar zaɓe ta ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen 18 ga watan Maris na 2023.
Kotun ta bayyana wannan hukunci ne, ta hanyar manhajar Zoom, cikin wani tsattsauran yanayin matakin tsaro.
Mai shari’a Oluyemi Akintan-Osadebay, shugabar kotun mai alƙalai guda uku.
Muna da tafe da ƙarin bayani
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)




