Labarai

Dole Yan Najeriya Su Shiga Matsin Rayuwa In Har Ana Son Komai Ya Daidaita – Tinubu

Tinubu ya ce dole yan Najeriya su shiga tsaka mai wuya idan har yana son gwamnatinsa ta samu damar gina tattalin arzikin da ya kamata.

Shugaba Bola Tinubu ya ce ya yanke hukunci mai tsauri don inganta tattalin arzikin Najeriya.jaridar Dimokuraɗiya na ruwaito.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce yana sane da ‘wahalar wucin gadi da manufofinsa na tattalin arziki da ‘yan Najeriya suka shiga ciki tun bayan cire tallafin man fetur.

Shugaban ya fadi haka ne yayin da yake gabatar da jawabinsa na farko a taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 78 da safiyar Laraba 20 ga Satumba, 2023.

Dole Yan Najeriya Su Shiga Matsin Rayuwa In Har Ana Son Komai Ya Daidaita - Tinubu
Dole Yan Najeriya Su Shiga Matsin Rayuwa In Har Ana Son Komai Ya Daidaita – Tinubu Hoto/Facebook

Tinubu ya ce ya cire tallafin man fetur mai tsada da cin hanci da rashawa, ya kuma yi watsi da tsarin ‘mummunan tsarin canjin canji’ a kwanakinsa na farko a ofis domin bunkasa tattalin arziki da kuma kwarin gwiwar masu zuba jari a Najeriya.

Hukunce-hukuncen manufofin shugaban kasar, musamman kawar da tallafin man fetur sakamakon haka ya jefa ‘yan Najeriya cikin mawuyacin hali na tattalin arziki yayin da farashin man fetur da sauran kayayyaki suka shiga sama.

Sai dai shugaban ya ce ya zama dole yan Najeriya su shiga cikin mawuyacin hali domin baiwa gwamnatinsa damar gina tattalin arzikin da ya kamata.

Ya ce ina tunawa da wahalhalu na wucin gadi da gyara zai iya haifarwa. Duk da haka, ya zama dole a bi ta wannan mataki domin kafa tushen ci gaba mai dorewa da zuba jari don gina tattalin arzikin da al’ummarmu suka cancanci.”

Don haka shugaban ya yi kira ga al’ummar duniya da su hada kai da Najeriya da Afirka ta yadda za su amfana.

Tambayar ba ita ce ko Najeriya a bude take don kasuwanci ba. Abin tambaya a nan shi ne, nawa ne da gaske a duniya ke budewa don yin kasuwanci da Najeriya da Afirka daidai da hanyar da za ta amfana da juna in ji Tinubu.

Ya ci gaba da cewa, dole ne cibiyoyin duniya da sauran kasashe da masu zaman kansu su dauki ci gaban Afirka a matsayin fifiko.







Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button