Shekau ya saki sabin Sautin Muruya inda yawa Sheikh Dr. Ahmad Gumi Barazana


Shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau ya saki sabon sautin Murya inda yakewa babban malamin addinin Islama dake jihar Kaduna, Sheikh Dr. Ahmad Gumi Barazana.
A hirar da yayi da BBChausa, Sheikh Ahmad Gumi ya bayyana cewa ‘yan ta’adda na amfani da Fulani saboda rashin cikakken Ilimin Addini suna tada zaune tsaye, wannan ne yasa ya shiga daji dan ya karantar da Fulanin.
Saidai a wata murya data bayyana a jiya, Talata da ta yi ikirarin cewa Shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau ne ta musanta cewa tana amfani da Fulani wajan aika-aikar ta inda kuma ya bayyana gargadi ga Shehin Malamin kan ya daina musu irin wancan zargin.
Hutudole ce na ruwaito.Shekau din ya bayyana cewa, basa amfani da kowabe irin mutane suna aikata laifuka amma sun san cewa akwai masu amfani da sunansu suna aika laifukan. Yace amma duk wanda yake son tarayya dasu, suna maraba dashi, kamar yanda eonsintelligence ta ruwaito.




