Raddi Mai Zafi Zuwa Ga Akan Ado Gwanja Akan Kalamansa Da Yayi Akan Annobar Covid 19 Daga – Indabawa Aliyu Imam
Ban tabbatar yaron nan mai siffatanta kanshi da mata wanda ake kira Ado Gwanjo yake ko gwanje tataccen jahili bane sai da na kalli raddin da yake wa hukuma akan daukan matakin dakile yaduwar cutar Covid-19 inda yake bayyana hakan a matsayin jahilci da rashin tunani.
Fasiki irin wannan yaro kazami wanda ke aikata badala a ban kasa wanda ya mayar da haramun abincinsa da shansa har shike fakewa da jam’in sallah yaci mutuncin al’umma ya kirasu jahilai, Allah na tuba babu tabbacin masu dabi’a irinta wannan yaro a same su suna Sallah guda biyar a cikin jam’i domin wakilan shaidan ne, basa tunanin mutuwa basa tsoron haduwa da Allah duba da munanan ayyukan da suke aikatawa.
A bayyane take wannan yaro ya fake da jam’in sallah ne domin ya nuna damuwa da bakin cikinsa akan rufe wurarensu da suke aikata badala da gwamnatin Kano tayi saboda gudun yaduwar annoba Coronavirus, bayan wannan babu wani dalili da har zai saka wannan yaro ya dinga siffanta mutane da jahilai marasa tunani, nan kuwa shine babban jahili, matsiyaci.
I.A.I