Labarai

SABBIN DOKOKIN WA’AZI A JIHAR KADUNA

1 – Za a kirkiro da ma’aikata da zata rika tantance wa’azuzzuka da kuma malaman da za su rika yin wa’azi a fadin jihar.
2 – Kowani malami sai ya mallaki lasisin yin wa’azi, musulmine ko Kirista.
3 – Za a kafa irin wadannan ofisoshi a kananan hukumomin jihar. Wadda sune za su rika mika wa hukumar sunayen malamai da Fastocin da za a tantance sannan kuma aba su lasisin yin wa’azi. Duk wanda bashi da lasisin yin wa’azi zai ko ga tasko.
4 – Daga yanzu sai dai ka saurari wa’azin ka a cikin mota, gida, cikin masallaci da da dakuna. Duk wanda aka kama ya kure wa’azi yana saurare zai kuka da kansa.
5 – Duk wanda ya kure karatu ko wa’azi ta lasifika daga karfe 11 na dare zuwa karfe 4 na safe zai yi kwanan kurkuku ko kuma ya biya taran naira 200,000.
6 – Sannan kuma duk wanda aka samu yana fadin kalamun batanci ga wani ko addini zai biya taran naira 100,000 ko kuma a garzaya da shi kurkuku ko kuma duka.
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button