Uncategorized

Sun fi kungiyar Boko Haram karfi! Wasu sababbin yan ta’adda sun bayyana a Najeriya, suna barazana ga gwamnati

Kasar Najeriya na fuskantar sabon barazana
– Sabon kungiyar yan ta’addan zasu hadassa tashin hankula daban-daban fiye da yan kungiyar Boko Haram
Kasar ta fara shirin yakar sabon kungiyar na yan ta’adda
Kwanan nan kasar Najeriya zata shiga alhini da kuma fuskantar tashin hankali sosai kamar yadda sabon kungiyar yan ta’adda ya billo kuma zasu iya halakar da kasar.
Sabon barazana
Gwanin ya bayyana cewa gaskiyar Magana shine akwai wani sabon abin tsoro dake dagawa cikin sauri a fadin duniya; wannan barazanar yafi nagarta kuma zai iya hadassa halaka fiya da kungiyar Boko Haram. Marubucin ya bayyana cewa sabon hanyar ta’addanci zai iya kasance w aba gaba da gaba ba amma a tashoshin yanar gizo.
Ku tuna cewa a shekara ta 2013 daraktan bincike na tarayya wato Federal Bereu of Investigation (FBI) yace yana sa ran barazana a tashoshin yanar gizo ya wuce bartazanar da kasa zata fuskanta a shekaru masu zuwa.
Yan ta’adda tashoshin yanar gizo
Sun fi kungiyar Boko Haram karfi
A shekara ta 2012, an rahoto cewa akwai kimanin Karin kaso 60 cikin 100 na hare-haren da aka kai ma yanar gizon gwamnatin tarayya.
Mu tuna cewa a Najeriya, an rahoto cewa an shiga yanar gizon hukumar zabe ta kasa (INEC) ba tare da izini ba a ranar da za’ayi zaben shugabancin kasa a shekara ta 2015.
Kuma irin wadanan hare haren-haren yana tashi daga bincike mai sauki da musun aiki zuwa ta’addanci mai yaduwa.
Aladenusi ya bayyana cewa kamar yadda mutane da baya basu ga zuwan kungiyar Boko Haram ba a shekaru 15 da suka wuce, idanuwanmu na iya rufewa kan yan ta’adda a tashoshin yanar gizo kan kayayyakin Najeriya.
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button