Kannywood

Yakamata gwamnatin najeriya ta rufe tik tok – sarkin waka Nazir M Ahmad

Advertisment

Yakamata gwamnatin najeriya ta rufe tik tok - sarkin waka Nazir M AhmadShahararren mawaƙin nan ɗan asalin jihar Kano, Naziru M. Ahmad da aka fi sani da Sarkin Waƙa, ya yi kira ga gwamnatin Tarayyar Najeriya da ta hana amfani da manhajar nan ta TikTok tun kafin lokaci ya ƙure.
Sarkin Waƙa ya bayyana haka ne a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Asabar .
“Ya kamata gwamnati ta dakatar da TikTok a Najeriya tun kafin lokaci ya ƙure”, in ji shi.
A iya jiya da daddare kimanin mutane 657 ne suka bayyana ra’ayinsu a ƙarƙashin wannan wallafa da Sarkin Waƙa ya yi, inda wasu suke goyon bayan sa wasu kuma suke sukar sa.
Mutane da dama dai a Najeriya suna da ra’ayin mahukunta su toshe manhajar TikTok sakamakon yadda wasu ‘yan mata ke amfani da ita ba ta yadda ya dace ba.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button