Labarai

kotu ta tabbatar wa gwamna Dauda kujerar gwamnan Zamfara

Advertisment

Matawalle ya sha ƙasa a kotun Koli, kotu ta tabbatar wa gwamna Dauda kujerar gwamnan Zamfara

Kotun Koli ta tabbatar wa gwamnan Zamfara, Dauda Lawal na Zamfara kujerar sa na gwamnan jihar.

A hukuncin da kotun Koli ta yanke a ranar Juma’a ta ce kotun Ɗaukaka kara sun tafka shirme a hukuncin da suka yanke da cire gwamnan da kuma sanar da sake zaɓe a wasu kananan hukumomi.

kotu ta tabbatar wa gwamna Dauda kujerar gwamnan Zamfara
kotu ta tabbatar wa gwamna Dauda kujerar gwamnan Zamfara Hoto/facebook: Dauda lawal

Maisharia Emmanuel Agim wanda ya karanta hukuncin a madadin alƙalan kotun ya bayyana cewa kotun ɗaukaka kara ba ta yi abinda ya dace ba ” Sabida haka kotun koli ta jaddada wa Lawal kujerar sa na gwamna Zamfara.

Wani labari : Ƴan bindiga sun kai wani ƙazamin hari wanda yayi sanadiyar rasuwar rayuka da yawa a kastina

Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun kashe Mai gari da ɗansa da wasu mutune taƙwas a kauyen Kukar Babangida da ke Karamar Hukumar Jibia a Jihar Katsina.

Kamar yadda Katsina Reporters ta samu, a daren ranar Laraba ne ’yan bindigar suka yi wa mutanen ki-san gilla, ciki har wani mai gadi da suka yi wa yan-kan rago.

Wani dan yankin da ya nemi a boye sunansa ya ce, zugar ’yan bindigar sun kai harin ne da misalin karfe 10 na dare, inda “suka ka-she mai gari Magaji Haruna da dansa Idris, tare da wasu mutane uku a gidansa.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button