Ya Kamata A Saka Sunana A Cikin Kundin Tarihin Duniya -Tinubu


Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewar zuwa yanzu ya kamata a saka sunansa a cikin kundin tarihin Duniya duba da irin yadda ya mayar da jahar Legas wata aljannar Duniya.
Shugaba Bola Tinubu ya ce ya cancanci a saka shi a cikin kundin tarihin duniya na Guinness saboda gyare-gyaren da ya yi tun hawansa mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023, shafin Liberty Tvr na ruwaito.
Tinubu ya bayyana cewa a lokacin da yake gwamnan jihar Legas a tsakanin shekarar 1999 zuwa 2007, ya kawar da jihar daga sifiri zuwa zama kasa ta biyar mafi karfin tattalin arziki a Nahiyar, inda ya kara da cewa irin nasarorin da ya samu ya sa ya zama shugaban kasa.
Ya bayyana hakan ne a yayin taron kasuwanci tsakanin Jamus da Najeriya karo na 10 a birnin Berlin na kasar Jamus.
Kalmominsa Ga waɗanda ke tsoron cikas iri-iri, ku dube ni; Na fito daga kamfanoni masu zaman kansu, kuma ni ɗaya ne daga cikin ku, Deloitte ya horar da ni. Na yi aiki a matsayin ma’ajin Exxon Mobil. Ƙayyade tsarin tafiyar da kamfanoni ta kowace hanya, kuma ina cikinsa.
Na yi mulkin Legas tsawon shekaru takwas a jere. A yau, zan iya bugun kirjina cewa jihar Legas tana kan gaba kuma ita ce kasa ta biyar mafi karfin tattalin arziki a Afirka, ta tashi daga sifiri. Wannan shi ne tarihin da ya kai ni ofishin shugaban Tarayyar Najeriya.
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)






