Labarai
Da dumi dumi : Buhari zai tafi London don duba lafiyarsa
Advertisment
Fadar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ta ce shugaban zai tafi Landan gobe Juma’a don duba lafiyarsa.


Mai taimakawa shugaba Buhari kan harkokin yaɗa labarai Femi Adesina ne ya sanar da hakan cikin wata gajeruwar sanarwa da ya fitar yau Alhamis,kamar yadda bbchausa na ruwaito.
Ya ce ana sa ran shugaban zai koma gida Najeriya a mako na biyu na watan Yuli mai kamawa.




