Labarai
Innalillahi wa inna ilaihi Raji’un!!! Allah Yayiwa Mahaifiyar Sheikh Kabiru Haruna Gombe Rasuwa
A yau ne ranar Alhamis munka samu labari daga shafin Jibwis Nigeria sun wallafa cewa
“Allah ya yiwa Hajiya Fatima Abdullahi Haruna mahaifiyar Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe Rasuwa a wani asibiti dake birnin Gombe.
Hajiya Fatima kai shekaru 75 ta rasu a hannun Dan nata Sheikh Kabiru Gombe, da misalin karfe 5:30pm na yamma. Za’a gabatar da sallar janazar ta a masallacin JIBWIS na Bolari a gobe juma’a da misalim karfe 1:30pm. Insha Allah.
Ibrahim Baba Suleiman
DG Social Media Nigeria”