Labarai
Gwamnan Gombe ya karrama wadda ta lashe gasar musabaƙa Alkur’ani da manyan kyaututtuka biyu


Advertisment
Gwamnatin Jihar Gombe a Nijeriya ta karrama matashiyar nan Hajara Ibrahim Ɗan’azumi, wadda ta lashe musabaƙar Alƙur’ani ta duniya ta mata da aka gudanar a ƙasar Jordan.
A yayin karramawan a ranar Alhamis, Gwamna Inuwa Yahaya na jihar ya miƙa mata kyautar naira miliyan biyar da kujerar Hajji da kuma sanar da ita ɗaukar nauyin karatunta da gwamnati za ta yi.
Kazalika an bai wa makarantar Islamiyyar da Hajara ke zuwa kyautar naira miliyan biyar.
“Na yabawa malamai da kuma dalibai gwaraza da sunka je sunka ciyo mana kyaututtuka da dauko matsayi wanda na tabbata idan jihar gombe mu ka tsaya a kowa ne fadi zamu iya zamowa zakuru, saboda muna da mutane haziƙai wanda kuma in sha Allahu suna mana abinda ya kamata”-inji inuwa yahaya.








![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)





