Labarai
Dokar shigo da kayan abinci ba tare da biyan haraji ba, za ta fara aiki mako mai kamawa – FG


Advertisment
A watan Yuli, Gwamnatin Tarayya ta amince da wani tagomashin kwanaki 150 da ba za a caji haraji ba wurin shigo da masara, shinkafa, da alkama a matsayin wani mataki na yaki da hauhawar farashin abinci a fadin kasar.
Wannan doka dai kamar yadda shugaban hukumar ta Kwastam ya sanar, za ta fara aiki a mako mai kamawa.
Da ya ke magana a taron shugabannin hukumomin tsaro a Abuja, Shugaban Hukumar Kwastam, Bashir Adeniyi, ya ce za a fara aiwatar da wannan dokar ta shigo da wadannan kayan abinci da zarar an gama shirye-shiryen da suka dace.
Bashir ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya da su dan kara hakuri inda yace wasu daga cikin wadannan kayayyaki da za a shigo da su yanzu haka za su wuce ba tare da haraji ba.
Dclhausa
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)





