Labarai
Ba’a ga watan sallah ƙarama ba a Nijeriya – Sarkin Musulmi


Advertisment
Kwamitin duban wata na fadar mai martaba Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar III ya ce ba a samu ganin jinjirin watan Shawwal ba a yau Litinin, 29 ga watan Ramadan.
Wata sanarwa ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin Farfesa Sambo Wali Junaidu ta ce Sarki Musulmi kuma shugaban majalisar koli ta harkokin addinin musulunci a Najeriya ya amince da rahoton kwamitin.



Saboda haka ya yi matsaya cewa watan Ramadan zai cika kwanaki 30 kuma ranar Laraba 10 ga watan Afrilu, ita za ta kasance 1 ga watan shawwal kuma ranar sallah karama a Najeriya
Ba wannan ne karon farko da ake yin Azumi talatin ba a Najeriya.
-BBC Hausa
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)




