Kotu ta baiwa Natasha Akpoti matsayin wadda ta lashe kujerar sanata a kogi


Kotun sauraron ƙararrakin zaɓe da ke zamanta a Jihar Kogi ta soke nasarar Sanata Abubakar Ohere a matsayin ɗan majalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta tsakiya.
Haka kuma kotun ta ayyana Natasha Akpoti-Uduagan ta jam’iyyar PDP a matsayin wadda ta lashe zaɓen da aka gudanar cikin watan Fabrairu.


Jaridar BBC Hausa na ruwaito jagoran kotun Mai shari’a K. A Orjiako ya ce an ƙara wa Ohere ƙuri’u a rumfunan zaɓe tara cikin ƙaramar hukumar Ajaokuta, yayin da kotun ta ce an rage wa Natasha ƙuri’u da gayya a hukumar zaɓen da kuma wasu rumfunan zaɓe uku da ba a shigar wa Natashan ba a ƙaramar hukumar.
Bayan da kotun ta kammala tattara alƙaluman ne ta ayyana Natasha ta jam’iyyar PDP a matsayin wadda ta yi nasara a zaɓen bayan da kotun ta ce ta samu ƙuri’a 54,074, yayin da ta ce Sanata Ohere ya samu kuri’a 51,291
Natasha Akpoti-Uduagan tayi fustin da nuna yiwa Allah godiya akan nasarar da ta samu.
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)



