Jerin matan Kannywood 8 da ake zargin sun yi bilicin bayan samun daukaka a harkar
A cikin wannan labarin za mu kawo muku sunaye, hotuna da kuma takaitaccen bayani dangane da jaruman Kannywood mata guda takwas (8) da ake zarginsu da sauya launin fatarsu bayan samun daukaka a fim.shafin labarunhausalabarunhausa na ruwaito
- Fati Washa
Jarumar ta dade ana damawa da ita a harkar fim din tun tana bayyana a matsayin ‘yar rawa har ta fara fitowa a tauraruwa a manyan fina-finai. Saidai an kula da yadda launin fatarta ya sauya bayan ta samu karbuwa a harkar.

2. Sadiya Kabala
Da forko ta fara bayyana a fina-finai, sai dain ta dena kasancewar ta fi mayar da hankali akan sana’arta ta siya da sutturu. amma ga wadanda su ka santa, za su kula da cewa launin fatarta ya sauya gaba daya.

3. Mansura Isah
Mansurah tsohuwar jarumar Kannywood ce kuma furodusa a halin yanzu. ita ce tsohuwar matar Sani Danja wanda ake zargin a masana’antar su ka rabu. Ita ma kwanan nan launin fatarta ya fara sauyawa.

4. Halima Atete
Haima ta dade tana cin zamaninta a masana’antar kasancewar ta iya hawa ko wanne matsayi aka sanya ta. Sai dai njama’a sun kula da yadda a hankali launin fatarta ya dinga sauyawa akan tsofaffin finafinanta.

5. Fati KK
Fati KK tsohuwar jarumar Kannywood ce wacce ta taka rawa sosai a fina-finan da ake yayi shekaru kusn goma da su ka gabata kamar Ban Sake ta ba, Mijina ne da sauransu. Bayan mutuiwar aurenta ne da ta dawo masana’antar da farar fata.

6. Maryam AB Yola
Maryam AB Yola tsohuwar jaruma ce wacce ta fara fitowa a shirin Adam Zango mai suna Nass, wanda daga bisani jarumin ya aureta. Sai dai bayan auren nasu ya mutu ne ya dawo masana’antar da farar fata wacce har ta kai ga wasu basu gane ta ba. Ya fito a shirin Hafiz, daga bisani ta fita gabadaya daga masana’antar.

7. Sadiya Haruna
Sadiya Haruna ma tsohuwar jaruma ce wacce ta samu matsaloli kwarai da wasu manya a masana’antar kamar Alhassan Kwalle, Teema Makamashi, Isah A Isah da sauransu. Ita ma launin ta ya sauya kwarai.

8. Umma Shehu
Umma Shehu ma tsohuwar jaruma ce, duk da dai dama tana da hasken fata amma ta kara musamman idan aka ga yadda ta sauya a cikin shirin Gidan Badamasi.
