Labarai

Tirkashi ! Anci tarar saurayi Miliyan 2.6 saboda yaki auren budurwasa

Wata kotun majistiret da ke da zama a Kumo fadar ƙaramar hukumar Akko a jihar Gombe ta yanke wa wani matashi hukuncin taran N2.6mn sakamakon yaudarar wata budurwar sa har na tsawon shekaru bakwai.
Budurwar ta yi ƙaran tsohon saurayin nata gaban kotun ne domin neman kotu ta bi mata haƙƙin ta tare da shaida mata cewa sun shafe shekara bakwai suna soyayya kwatsam sai ta samu labarin zai auri wata da ba ita ba.
Tuni alƙalin wannan kotu ya umarci wannan saurayi da ya biya ta zunzurutun kuɗi har N2.6m ko kuma ya aureta ko ya tafi gidan gyaran hali na tsawon shekaru 8.
A bangaren saurayin, ya zabi ya fasa auran wacce akasa musu rana domin aurar tsohuwar budurwar sa da ta yi ƙarar sa.
Lallai idan har kotuna za su rika yin irin wannan hukunci samari za su rage yaudara.
Daga: Yushau Garba Shanga

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

One Comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button