Za a bude layukan wayoyin salula a Zamfara
Gwamnan jihar Zamfara, Bello Mohammed Matawalle, ya ce nan da ranar Talata za a bude layukan wayar salula a fadin jihar.
Ya bayyana haka ne a wurin zaben shugabannin jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ranar Asabar.
A farkon watan Satuba ne aka katse layukan a wani mataki na dakile hare-haren ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane.
Bbchausa ta ruwaito Sai dai a kwanakin baya an bude layukan wayar salula da intanet da aka katse a Gusau, babban birnin jihar.
Matawalle ya kara da cewa za a sake bude kasuwannin da aka rufe sakamakon matsalar tsaro.
“Bayanan da muka samu sun nuna cewa an samu raguwar matsalolin tsaro a yankunan jihar nan, kuma nan da Litinin ko Talata za mu sake bude layukan wayoyin salula, kowa da kowa zai samu damar yin waya,” in ji gwamnan


