Labarai

Dr Ibrahim Jalo Jalingo Yayi Martani Mai Zafi Kan Wannan Fitsara

Advertisment

Dr ibrahim jalo jalingo yayi martani mai zafi wanda dole saboda irin wannan abubuwan suna jawo fushin ubangiji.
Inda ya wallafa a shafinsa kamar haka

1. Lalle irin yadda amare ‘ya’yan musulmi suke yin shiga ta nuna tsiraici a mahangar Musulunci sannan kuma su dauki hotunansu cikin wannan shiga ta fitsara su watsa wa Duniya, abin takaici ne matuka. Kuma abu ne da zai iya jawo hushin Allah a kan al’ummar Kasa.

2. Lalle mun ga irin wannan fitsara, da saba Shari’ah, a ‘yan shekaru kadan da suka wuce daga wata ‘yar shugaban kasa, muka kuma sake ganin irinta daga wata ‘yar gwamna, ga shi a yau kuma muna ganin ta daga wata ‘yar babban sarki!!

Zahra NasirU Ado Bayero Amaryar Yusuf Buhari

3. Muna rokon Allah Madaukakin Sarki cewa kada Ya kama mu da laifin da wawayen cikinmu suke aikatawa. Ameen.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button