WHO ta cire Najeriya cikin kasashen Da zata baiwa Tallafin rigakafin cutar Coronavirus/COVID-19


Hukumar da zata baiwa kasashe mabukata tallafin cutar Coronavirus/COVID-19, COVAX Global Initiative wadda ke karkashin Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta cire Najeriya daga jerin kasashen da zasu sami tallafin rigakafin cutar Coronavirus/COVID-19.
Gwamnatin tarayya a baya ta fadi cewa, zata samu tallafin Rigakafin cutar Coronavirus/COVID-19 100,000, saidai WHO kasashe 4 ne kawai daga Africa ta amincewa au karbi Rigakafin, sune kasar Africa ta Kudu, Cape verde, Rwanda, da Tunisia.
Kamar yadda Hutudole na ruwaito.Wakilin WHO a Africa, Dr. Matsidiso Moeti ya bayyana cewa, ba zasu bayar da rigakafin cutar Coronavirus/COVID-19 ba inda za’a lalatashi. Yace kasashen da basu bada tabbacin cewa suna da tsarin da zasu yiwa rigakafin kyakkyawar ajiya ba an fitar dasu daga wanda za’a baiwa tallafin.



