Labarai

ABIN AL’AJIBI!| An Yanke Wutar Gidan Tsohon Shugaban Kasa Shehu Shagari Saboda Bashi

Advertisment

Hukumar rarraba wutar lantarki ta Kaduna ta yanke wutar gidan tsohon shugaban kasa marigayi Shehu Shagari saboda bashin naira miliyan 6 da ake bin gidan.
A ranar 28 ga watan Disamba ne 2018 tsohon shugaban ya rasu yana da shekara 93.
Jaridar DAILY NIGERIA ta rawaito kakakin kamfanin, Abdulaziz Abdullahi na cewa ba a biyan kuɗin wutar tun bayan mutuwar marigayi Shagari.
Kakakin ya kuma shaida wa jaridar cewa an basu wa’adi ko ɗaga musu ƙafa domin biyan kuɗaɗen da ake bin su kafin a yanke wutar.
Wani jami’in gwamnatin jahar Sokoto wanda ya bukaci a sakaya sunansa ya ce babu adalci idan aka ɗaurawa gwamnati laifi kan yanke wutar, a cewar Jaridar.
Allah sarki duniya, lallai kasar nan duk wanda yayyi aiki akan gaskiya sai dai ya jira sakamakonsa a lahira, amman da zarar ya mutu za a manta da shi, za a manta da ya’yansa.
Tabbas wannan abin kunya ne ga gwamnatin jahar Sokoto da kuma masu kudin jahar Sokoto. Majiyarmu ta samu labarin ne daga nasara.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button