Uncategorized

Shin Watanni Nawa Miji Zai Iya Kauracewa Matarshi Ta Sunna ?- Dr Jamilu Yusuf Zarewa

Advertisment

Shin Watanni Nawa  Miji Zai Iya Kauracewa  Matarshi  Ta Sunnah ?

Tambaya:
Tambaya  ita ce؛ shin Tsawon wani lokaci ne ya halatta miji ya kaurace wa matar shi ta sunna kuma wani Mataki ya dace ta dauka in har ya wuce period din da sharia ta halatta?.

Amsa:
Wa’alaykumussalam, Ya halatta ya kaurace mata tsawon watanni hudu kamar yadda Allah ya fadi a suratul Bakara aya ta: 226. 

Bai halatta ya wuce hakan ba, in ya koma da kansa ya cigaba da saduwa da ita to Allah mai gafara ne game da abin da ya wuce, in har ba zai koma ba bayan watanni hudu sai ya sake ta kamar yadda aya ta 227 a cikin surar ta nuna hakan.                          

In ya ki komawa ya sadu da ita kuma ya ki saki sai taje wurin Alkali don ya bashi zabi tunda wata hudu ya cika ko ya dawo mata ko kuma ya sake.                           

Allah ne mafi Sani

Amsawa

Dr Jamilu Yusuf Zarewa

10/02/2017

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com
Advertisment






Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button