Masha Allah, Aminu Saira Ya Samu Karuwar ‘Ya Mace


Wanda yayi wannan fastin din wannan sanarwa a shafinsa na sada zumunta a Instagram ga abinda ya wallafa.
“Alhamdulillah, Masha Allah. Allah ya Azurta Mu da Samin Karuwar “Ya Mace, Mun sanya mata Suna AISHAt Aminu Saira. (AMIRA) Allah ya raya ta cikin Aminci, Allah yasa ta albarkaci musulunci da musulmai.”
Malam aminu saira babban mai bada umurni ne a masanaantar kannywood wanda shi ya bada umurni fim din dan marayen zaki, ahalil kitabi fina finai dai da dama wanda kuma shine mai bada umurni sabon shirin da ake mai dogon zango wanda tashar arewa24 tv ke haskakawa da kuma shafin youtube channel mai suna saira movies tv.
Ga hotunan aishat aminu saira kanwar maza.







