Labarai

DA DUMIDUMI: Gwamnatin Tarayya Ta Gindaya Sharruda Guda Shida Na Komawa Makarantu

Daga Haji Shehu

Bayan shafe wata da watanni makarantu suna kulle sakamakon annobar cutar corona, gwamnatin tarayya ta bayyana wasu sharruda guda shida da kowacce makaranta za ta bi kafun a bude makarantun.

A cewar gwamnatin, kowacce makaranta sai ta samar da waɗannan ababe.

 1) Wajen wanke hannu
2) Na’urar gwajin dumamar jiki
3) Na’urar kashe kwayoyin cuta a kowacce mashigar makaranta da kuma manyan wurare kamar su, Babbar kofar shiga, dakin kwanan dalibai, dakunan karatu, ofis da sauransu.
4) Kowacce makaranta za ta yi feshin kashe kwayoyin cuta a harabarta.
5) Dole ne kowacce makaranta ta kula da tsafta matuka.
6) Tabbatar da tazara a dakunan karatu da ofisoshi.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button