Uncategorized

AMFANIN ZOGALE GOMA SHATAKWAS (18) GA JIKIN DAN-ADAM

AMFANIN ZOGALE GOMA SHA
TAKWAS (18) GA JIKIN DAN-ADAM
==========================
Ana Bukatar Jama’a su yada wannan Post zuwaga Sauran Al’umma domin Qaruwa da Juna.
.
1- Ana dafa ganyen zogale da zuma a
sha kamar shayi domin maganin Olsa (ulcer).
.
2- Ana shafa danyen ganyen zogale
akan goshi
domin maganin ciwon kai.
.
3- Ga wanda ya yanke ko ya sare ko
wani karfe ya ji masa ciwo, zai shafa danyen
ganyen zogale
inshaAllah jinin zai tsaya.
.
4- Ga mai fama da kuraje a jiki, ya
hada garin
zogale da man zaitun ya shafa.
.
5- Ana sanya garin zogale akan wani
rauni ko
gembo domin saurin warkewa.
.
6- Sanya garin zogale a cikin abinci
yana
maganin hawan-jini da kuma karama mutum
kuzari.
.
7- Ana dafa ganyen zogale tare da sa
kanwa ‘yar
kadan domin maganin ciwon
shawara.
.
8- Ga mai fama da ciwon ido zai diga
ruwan
danyen zogale, haka ma mai fama da
ciwon
kunne.
.
9- Macen da ke shayarwa ta dafa furen zogale da
zuma dan karin nono.
.
10-Wanda ke fama da yawan fitsari
wato cutar
Diyabetis ya rinka shan furen zogale
da citta kamar shayi.
.
11-Idan aka tafasa furen zogale da
albasa aka
sha kamar shayi yana maganin
sanyi.
.
12-Haka ma cin danyen zogale yana maganin
tsutsar ciki ga yara.
.
13-Ana daka ganyen zogale da
‘ya’yan baure a
sha da nono ko kunu yana maganin
ciwon hanta.
.
14-Ga mai fama da sanyin kashi ko
wani kumburi
zai soya ‘ya’yan zogale a daka su
sannan a hada
da man kwakwa (man-ja) sai a shafa.
.
15-A daka zangarniyar zogale da ‘ya’yan da ke
ciki tare da karanfani, citta, masoro
da kuma
kimba domin karin karfin da namiji
da sa masa
kuzari, haka kuma yana karawa mata nishadi.
.
16-A daka saiwar zogale da ‘ya’yan
kankana a
sha da nono yana maganin tsakuwar
ciki
(Apendis).
.
17-Haka kuma idan mutum yana
fama da ciwon
Aids zogale kan radadinshi ta hanyar
shan ruwan
dafaffen zogale.
.
18-Haka kuma mai fama da Typhoid da malaria
da kuma ciwon basir ko shawara, zai
iya yawaita
shan ruwan dafaffen zogalen domin
samun sauki.
.
Ana Bukatar Jama’a su yada wannan Post zuwaga Sauran Al’umma domin Qaruwa da Juna.
.
Allah ya kara mana lafiya kuma ya bamu ikon
gode masa da ita ta hanyar aikata
umurninsa da
nisantar abinda ya hana
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button