Mun san wadanda suka dauki nauyin zanga-zangar da aka yi a PDP ta fadawa Tinubu


Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa ta san wadanda suka dauki nauyin zanga-zangar #EndBadGovernance da ta da akayi a watan Agusta.
Wasu ‘yan Nijeriya da kungiyoyi sun fito kan tituna a garuruwa da dama tsakanin ranakun 1 zuwa 10 ga watan Agusta domin nuna adawa da wahalhalun da ake fama da su a kasar.
Da yake jawabi ga manema labarai a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja a ranar Litinin, Debo Ologunagba, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar PDP na kasa, ya bayyana cewa yunwa ce ta dauki nauyin zanga-zangar, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta kama yunwa ba ‘yan Najeriya ba.
Ologunagba ya yi magana ne a kan yadda aka kama shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajearo.
Kakakin PDP ya ce akwai bukatar a yi taka-tsan-tsan An yi zanga-zanga a kasar nan, gwamnati ba ta yi komai ba.
Dclhausa
![[Bidiyo] Ni na haɗa auren G-Fresh da Alpha Charles – Jaruma Babiana](https://i0.wp.com/hausaloaded.com/wp-content/uploads/2024/12/Picsart_24-12-25_12-05-31-313-scaled.jpg?resize=220%2C150&ssl=1)




