Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Kano ta saka dokar hana fita ta awanni 24

Advertisment

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ne ya ayyana dokar a taron manema labarai da ke gudana a gidan gwamnati a halin yanzu.

Ya ce an saka dokar ne domin a dakile sace-sace da fashe-fashen kayan gwamnati da na al’umma da wasu ɓatagari ke yi a ƙarƙashin zanga-zanga.

Ya ce wasu ƴan siyasa ne da ba sa don ci gaban Kano ke daukar nauyin yan daba wadanda su ka dake da zanga-zanga su ka fara kai hare-hare.

Ya kuma umarci jami’an tsaro da su gaggauta fara aiwatar da dokar nan take.

Advertisment

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Advertisment
Back to top button