Labarai

Gwamnatin Kano ta kaddamar da kwamitin aiwatar da mafi karancin albashi

Advertisment

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da kwamitin ba da shawara kan sabon mafi karancin albashi, biyo bayan amincewar da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi na sabon mafi karancin albashi na N70,000.

Kaddamarwar ta gudana ne a gidan gwamnatin jihar, wanda mataimakin gwamna Aminu Abdussalam Gwarzo ya jagoranta a madadin gwamnan.

Kafa kwamitin ya zo ne sa’o’i 48 kacal bayan amincewar shugaban kasa. Jihar Kano dai ta zama jiha ta farko a Nijeriya da ta kafa irin wannan kwamiti.

Wani labari: Ndume ya ki amincewa da sabon ofishin da aka bashi a majalisar dattawa

Advertisment

Sanata mai wakiltar Borno ta kudu a majalisar dattawan Nijeriya, Mohammed Ali Ndume, ya yi watsi da sabon ofishin da kwamitin ayyuka na majalisar dattawa ya bashi.

Ndume, a wata wasika da ya aike wa shugaban kwamitin ayyuka na majalisar dattawa a ranar Talatar nan, ya ce ofishin da aka ba shi bai nuna girmansa da matsayinsa a majalisar dattawa ba.

Wasikar mai dauke da sa hannun babban sakataren sa,Yati Shuaibu Gawu, ta ce: “An umurce ni da in sanar da ku cewa, Sanata Mohammed Ali Ndume, ya ki amincewa da ofishin da aka bashi mai lamba 3.10 da kwamitin ayyuka ya yi.

Idan ba a manta ba a kwanakin baya ne aka tube Ndume daga mukaminsa na babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, biyo bayan sukar da ya yi wa gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Advertisment
Back to top button